Haske New hausa Novels Document Compelet writing by Salma A. Isah


BOOK Contact INFORMATION FOR THIS BOOK IN THE YEAR
BOOK HASHE
AUTHOR Salma Ahmad Isa
UPLOADER MRS SUFI
IMAGE GRP SUFI GRAPHICS
SIZE 1.MB
File TXT
Date 02 MAY 2024
Group ZAUREN SUFI NOVELS
TAGES LOVE STORY

DESCRIPTION

  • He was standing in front of the glass wall in the hotel room he stayed in, his eyes fixed on the beautiful buildings in the city of Abu Dhabi, the city itself is beautiful to him, especially at night. Although he went to dance on stage, sing and shout, but he does not feel tired in his body, tomorrow he will return to his country of inheritance, that is Nigeria.
  •  The ringing of his phone on the bed made him look back. Then he slowly started walking towards the bed, he reached his hand and took the phone. 'Umma' is the name floating on the screen. With a small smile on his face he picked up the phone. Sallama started to say in his sweet voice. After that, he was greeted on the phone and greeted the woman respectfully.
  •  "TAUQEER will you come back tomorrow?"
  •  His head slowly turned around.
  •  "Thank God Ummah!"
  •  "May God bring you back safely, may God bless you "Amen"
  •  He answered, removing the phone from his ear, the phone cut off, he brushed his hair from front to back, letting out a breath of air from his mouth.
  •  He slowly sat on the edge of the bed and shook his head, before he slowly lay down on the bed, he was sleepy, but the sleep escaped his eyes.
  •  *Agha Mansion, No.854, Lekki pahse 1, Lagos State, Nigeria.*
  •  It is a big house, which can be called as an independent house, the building of the house responds to the name of the house. From the outside, the house is just a sight to behold, just step outside and put your foot in the first gate of the house.
  •  From the end of the gate of the house, you will come across a tarmac, which will connect you to the inside of the house. The beautiful garden of the house is at the beginning of the house, before you find the actual entrance to the house. The house is a one story building.
  •   When you see the house, you know that this is stronger than a single person, although the building is not modern, but the materials that have been poured into it are new, it has been done, this shows that the owners of the house take care of it properly. should.
  •  That is Agha Mansion. It is a single family home. Agha Muhammad is the real foundation of the family. He and his wife Fariya. From Agha to his wife Fariya, they are all Yola fulani.
  •  God blessed them with six children: Faruq Agha, he is the eldest of their children, he is the owner of A. FOODS NIG LTD. A major company that is well known throughout Nigeria, the processing and importation of food products.
  •  He is Mas'ud Agha, he is a soldier, he holds the title of General.
  •  Then Tayyab Agha, he was an orthopedic surgeon, and he owned his own hospital.
  •  What followed him was Muzamil Agha, and he followed the footsteps of his brother Faruq, who did their business together.
  •  Then their eldest daughter, and the only woman among them, Abida, who got married recently. And she lives in Abuja with her husband and children.
  •  And all these people live in Agha Mansion. Because there is no one among them who has not raised a family.
  •  One Faruq's wife, her name is Maryam, and the children of the house call her Umma, a woman who is kind and knowledgeable, has foresight, and feels for the poor. His four children with her, TAUQEER is the eldest, they call him Junior, because he took the name of Maryam's father. Then Jamal. What is next for him is Iqra, then their youngest Aabis.
  • Mas'ud also has one wife, her name is Hafiza, the children call her Amma. She is a careless girl, she has nothing to do with the family, no matter what is done, she is on the sidelines, she doesn't care about anyone. She had four children, her first born two sons, Tajuddin and Saifuddin, then Muhammad, who was married to Hammad, and the younger Khabir.

TSAKURE 

Wata matace ke tafe cikin sassarfa, sanye take da atamafa kalar ruwan goro, wanda akewa laƙabi da me dalma. Hannunta riƙe da wani abu, wanda ke duƙunƙune cikin zani.
Kanta ta ɗan ɗaga ta kalli sararin samaniya, ta ga yanda hadari yake gangamuwa, ga kuma iska me ƙarfi da aka fara, sai cida da tsawa da ake har da walƙiya.
Ƙafafuwanta ne suka taka birki, a lokacin da ta kawo gaɓar ruwan shiga yankin Makoko. Tarin kwale-kwalen dake bakin ruwan ta kalla, sannan ta kalli abun da ke hannunta. Hawaye na bin fuskarta ta girgiza kai tana faɗin.
“Ba zan iya aikata haka ba!”
Sai kuma ta shiga juyawa tana kallon kewayen wurin da take, babu kowa sai gilmawar karnuka. haka ta nufi wani kwale-kwale dake cikin tarin kwale-kwalen dake wurin, ta shiga cikin kwale-kwalen ba tare da tsoro ba, ta tsuganna tana aje abinda ke hannunta.
Kafin a hankali ta kai hannunta kan zanin, ta buɗe shi, nan take fuskar jaririya sabuwar haihuwa ta bayyana, don da alama yanzu ta zo duniya, saboda ko jinin haihuwarta bai bushe daga jikinta ba. Fuskar yarinyar ta ƙara rufewa da zanin, ta ɗora wata sarƙar ƙafa a kan zanin. Sannan ta miƙe ta fita daga cikin kwale-kwalen. Ta dawo ta bayansa, ta shiga turashi cikin ruwan, har ta samu nasarar turashi gaba ɗaya. A kan idonta kwale-kwalen ya shiga yawo a kan ruwan. Ya na nufar gidajen katakwayen dake saman ruwan. Sai da ta share ƙwallar idonta tukkuna, sannan ta juya da gudu ta bar wurin.
Ma somin ƙaddarar kenan, a ganinta ta kawo ƙarshen matsalolin, tun da har bata kashe jaririyar ba kamar yanda aka umarceta. Tun da har yarinyar ta yi nesa da gidan, wata ƙila komai zai ƙare.
Tana wannan tunanin ne ba tare da sanin cewa yanzu ne komai zai fara ba, dan kuwa barin yarinyar da ta yi a raye, shi ne musabbabbin buɗewar ƙofofinsu wasu tarin ƙaddararo da ko ita kanta bata san da aukuwarsu ba. Saboda ta kashe maciji ne batare da ta sare kansa ba. A yanzu ne komai zai fara!.
*Present day...*
*Shekara ta 2024.*
*Makoko, Lagos State, Nigeria.*
*06:30 na Safe.*
“Wai Shola ba za ki fito ki tafi wurin aiki ba?... Kin kusa makara fa!”
Cewar wata baƙar mata cikin harshen yarbanci, yayin da take zaune a kan dandaryar katakon da aka kafa ginin gidanta da shi. Daga can cikin ƙaramin ɗakin gidan, muryar wata matashiya ta bata amsa cikin faɗin.
“Takalmi nake sakawa Gigi!”
Matar ta girgiza kanta tana dawo da dubanta kan mijinta dake kwance a gefenta. Fuskarsa ta ɗan leƙa ganin idonsa a rufe, zatonta bacci yake. Amma a zahirin gaskiya ba baccin yake ba, idonsa biyu, tunanin rayuwa ne yasa shi a gaba.
Damuwar halin da gidansa ke ciki ita ce ta sako shi a gaba, ba dan 'yarsa ɗaya Shola ta duƙufa wurin nemo kuɗin da zasu ci abinci ba, da tuni gidan nasu ya jima da durƙushewa. A da shi ne yake kula da gidan, amma tun bayan iftila'in hatsari da ya afka masa riƙon gidan nasa ya koma hannun 'yarsa DIYA, wanda sukewa inkiya da SHOLA.
“Ga ni na fito”
Cewar Shola, bayan da ta fito daga tilon ɗakin gidan nasu, a tare suka dubeta, daga Gigin har mijinta da ya buɗe idonsa.
Sanye take cikin wani baƙin wando me faɗi, sai wata farar oxford shirt. Kanta yafe da baƙin gyale. Ƙafafunta sanye da fararen canvas da suka fara jin jiki. Wannan shi ne kayan da ta saba sakawa idan zata je wurin aiki. Fara ce sosai, tana da matsakaicin jiki, idan za ka mata adalci, a kallon farki idan ja mata za ka kirata da bafulatana.
Gigi ta yi murmushi.
“Ga guntuwar shinkafar jiya, ki ɗan taɓa kafin ki tafi”
Shola ta girgiza kanta tana sauƙowa daga kan mattattakalan katakon gidan nasu.
“A'a Gigi, ni idan na ci ku me za ku ci?, kawai ku ci, idan na je wurin aiki zan samu abun da zan ci”
Gigi ta miƙe tana fitowa daga gidan katakon nasu, ta tsaya kusa da Sholan dake kiran sunan Ekene, wanda yake zaune a gidan dake gaban nasu, dan ya zo ya fitar da ita bakin gaɓar ruwan unguwar tasu, dan ba'a zirga-zirga a unguwar sai da kwale-kwale.
“Ya kamata ki taɓa wani abun Shola”
Diya ta juyo ta kalleta.
“Karki damu da ni Gigi, ko biredi ne zan siya na ci, ke de ki kula, na bar miki ɗari biyar a ɗaki, wata ƙila za ku buƙace ta”
Gigi ta yi murmushi tana shafa kanta, tare da saka mata albarka.
“Shola ga ni”
Cewar Ekenen da take kira, bayan da ya fito daga ɗakinsu na katako.
“Na kusa makara Ekene! Ka zo ka fitar da ni”
Ta faɗi tana dubansa. Saida ya ɗaga busassun hannayensa ya yi miƙa, kafin ya sauƙe yana jan wata baƙar tsohuwar singlet da ke rataye a jikin wata gwafa ta gidansu. Sannan ya zagaya ta inda kwale-kwalensa yake, ya cinto shi daga jikin wani ƙarfe da ya ɗaureshi, sannan ya shiga yana ɗaukan marar kwale-kwalen, ya zagayo da shi har zuwa ƙofar gidansu Shola. 
Shola ta yi wa Gigi sallama, sannan ta hau kwale-kwalen. Ekene ya fara tuƙasu. Diya ta ci gaba da kallon irin wahalar rayuwar da ake a yankin nasu. Kaf gidajen yankin na katako ne, kuma a saman ruwa suke, dan gaba ɗayan unguwar ma kanta malale take da ruwa, shi yasa ko ina zaka sai ka hau kwale-kwale. 
Sosai ake shan wahalar rayuwa a yankin, yawancin mazaunan yankin masu zuwa cirani ne, sai 'yan gudun hijara, da kuma wanda ƙaddara ta zama silar zuwansu wurin. Yankin nasu ya haɗa tarin ƙabulu, da kuma mutane masu mabanbanta halaye. Kowa ta kansa yake a wurin, babu ruwan wani da rayuwar gidan wani.
“Mun iso!”
Cewar Ekene, sanda suka iso bakin ruwan. A hankali ta miƙe, hannunta riƙe da jakarta. Godiya ta masa tana fita daga kwale-kwalen. Hanya ta yanka ta so ma tafiya. Kafin ta samu isowa tashar bus ɗin da ta saba hawa.
Tafiyar munti 55 ce ta kaita cikin Victoria Island. A wani bus stop suka tsaya, ta fito daga motar bus ɗin, tare da sauran mutanen da suka shiga motar. A ƙafa ta fara takawa, har ta iso Cactus restaurant. Wurin da take aikin raba abinci kenan.
Memakon ta shiga ta ƙofar gaba kamar yanda kowa ke shiga, sai ta zagaya zuwa backyard ɗin ginin restaurant ɗin, ta shiga ta ƙofar kitchen ɗin restaurant ɗin dake baya.
“Shola sai yanzu kika iso?”
Ɗaya daga cikin masu girkin wurin ta tambayeta, yayin da take ƙoƙarin saka apron ɗinta dake rataye a jikin wani hook. Zaren apron ɗin ta gama ɗaurawa tana faɗin.
“Eh Wallahi, sai yanzu na samu isowa”
“Diya! Diya!”
Tun daga nesa suke jiyowa muryar Orisa cikin ƙwalla kiran sunan Diya. Kafin Diyan ta amsa, Orisa ta bayyana a cikin kitchen ɗin.
“Wai ya aka yi kika makara?.... MD ya zo yana ta faɗa!”
Orisa ta faɗa mata cikin harshen yarbanci, Diyah ta saka jakarta cikin wata loka tana amsa mata da.
“Yau ban farka da wuri ba ne!”
“Lalle kam, ke har wani lokacin miƙe ƙafa ki yi bacci kika samu?”
Orisa ta tambaya. Diya ta miƙe tana kallonta.
“Orisa mutum idan be huta ba ai sai ya samu matsala, mu yini muna aiki mu koma gida kuma a ce ba za mu yi bacci ba?”
Orisa ta gyaɗa kanta.
“To yanzu dai ba zan ce za ku tsaya kuna yi ba. Ga wani plate ɗin brown spaghetti can, ki ɗauka ki kai teburi na sha takwas”
Cewar Ifunaya, shugabar sashensu na masu kaiwa abinci.
“Ok”
 Diya ta amsa tana raɓa Orisa, plate ɗin brown spaghettin ta ɗauka ta ɗora a kan wani tray me kyau, ta nufi ƙofar shiga cikin restaurant ɗin.
Da misalin ƙarfe tara na dare ta kamo hanyar dawowa gida, bayan da ta tashi daga aiki, hannunta na dama riƙe da wata farar leda. Kafaɗarta kuma saƙale da jakarta. Kasancewar a yankin nasu ba ko ina ne me wutar nepa ba, yasa take amfani da hasken wayarta, wurin haska hanya.
Kuma har zuwa lokacin akwai sawun mutane a waje. Ranta ne ya ɓaci asanda ta iso bakin ruwan yankin nasu, ta iske babu masu yin fito, sai de tarin kwale-kwale a bakin wurin. Ga shi Ekene tsabar talauci da ya masa kanta ko waya ba shi da ita, bare ta kirashi dan ya zo ya fitar da ita. 
Haka ta duba ɗaya daga cikin kwale-kwalen da ta san me shi, ta fara tura shi zuwa cikin ruwan, kafin ta ɗale ciki tana ɗaukan marar fiton sa, ta fara tuƙa kwale-kwalen. 
Ganin hasken fitila kunne a tsohon gidansu da ya kusa durƙushewa ya sa ta fahimci cewar har yanzu basu kwanta ba. A kan matakalar katakon ƙofar gidan nasu na ƙarshe ta dire,sannan ta ɗaure kwale-kwalen a jikin wani ɗan katako dake jikin gidan nasu.
Sannan ta ɗebi kayanta da ta aje su a cikin jirgin, ta fara taku a hankali, saboda yanayin jimawar da katakon ginin gidan ya yi, ya sa ba sa taku da ƙarfi, dan abu kaɗan ne zai iya sawa ya karye, saboda wasu wuraren ma sun karye ɗin.
A tilon ɗakin nasu ta tarar da su, Gigi na zaune tana wa Papi firfita, sun kunna mosquito coil, sai wata dundurusun fitilarsu mara haske sosai dake ci. Ɗakin babu komai sai wasu lamitssatssun katifu guda biyu, dake yashe a ƙasan ɗakin, sai 'yan wasu jakkukkunansu na kaya. Dan basu cika tara tarkace a ɗakin ba, gudun kada katakon gidan ya ɓalgace.
“Ba ku yi bacci ba?”
Ta tambaya tana cire viel ɗin jikinta, Gigi ta kalleta tana faɗin.
“Tukunna dai, zafi ne ya hana mu kwanciya”
Diya ta dawo bakin ƙofar ɗakin nasu, ta ɗauke labulen ɗakin, saboda iska ta ɗan samu ta shigo ciki. Ta dawo ta ɗauki kwandon soso da sabulunta, ta fita waje.
Ɗan siririn banɗakin gidan ta shiga, da wani ruwa rabin bokiti ta samu ta ɗan yi wanka, sannan ta fito, jikinta ɗaure da zani, ta dawo ɗakin ta saka wata doguwar rigarta. Sannan ta zauna kusa da Gigi, tana jan ledar da ta shigo da ita.
“Papi na samu kuɗin siyan maganinka, amma ɗaya aka samu, sai a yi maneji”
Papi ya kalli tilon 'yar tasa, ƙwalla na shirin taruwa a idonsa, a shekarun da suka wuce ya tsinceta, shi ya kula da ita har girmanta, sai ga shi a yau ita ce take kula da shi, rayuwa kenan.
“Allah ya miki albarka Shola”
Ta sunkuyar da kanta tana amsa masa da amin.
“Yau me kuka ci da rana?”
Ta faɗi tana fitar da sauran kayan da ke cikin ledar, Gigi ta aje muficin hannunta tana faɗin.
“Taliya muka ci”
Robar da ta zubo sauran abincin da ya yi saura a restaurant ɗinsu ta fitar, dan idan abinci ya yi saura su ake rabawa.
“Ga abinci na zo da shi, Papi ka tashi sai ka ci”
Kansa ya girgiza mata.
“A'a Shola, ke da Giginki dai ku ci... Amma ni na ƙoshi”
Shola ta ɓata fuska.
“Idan baka ci ba ni ma ba zan ci ba”
Da sauri ya yunƙura ya zauna.
“Yi haƙuri to, zan ci”
Ta ɗan yi dariya tana kallon Gigi, Gigi ta yi murmushi tana shafa kanta.
Haka suka gama cin abincin tana basu labarin abubuwan da suka faru da ita yau a waje, wani abu da tun tana yarinya take yi, duk inda zata je ta dawo, sai ta basu labarin abun da ya faru da ita a wurin.
Ko da suka gama cin abincin sai ta ɗauki katafarta ta fita da ita rumfar ƙofar gidan nasu, ta shimfiɗata, ta kawo wani jemammen bedsheet ta shimfiɗa. Kafin ta kawo wani fatattakkakken net ta ɗaura. Ta shiga cikin shimfiɗar tata ta kwanta.
Tana hasashen yanda ranar gobe zata kasance, wannan ita ce rayuwar da take gudanarwa tare da iyayenta, rayuwar tasu me wahala ce, amma kuma suna cikin farinciki. Shekaru uku kenan da fara aikinta, kuma a shekaru ukun da suka wuce ne, Papi ya samu hatsarin mota, sannan tun lokacin ƙafarsa ta samu matsala. 
Har aka buƙaci wasu maƙudan kuɗe wurin mata aiki, Kasancewar basu da su, ya sa suka dawo gida suka zubawa saratar Allah ido.
Ganin zaman ba zai kaisu ba ya sa ita Diyan shiga cikin gari neman aiki, kuma cikin nasara ta samu, da shi ne suke iya rayuwa a yanzu.

{getButton} $icon={download} $text={DOWNLOAD NOW}

Post a Comment

Previous Post Next Post