Karni Uku book 1 by Mansur Usman Sufi


BOOK CONTACT INFORMATION THE BOOK FOR THIS YEAR 2022
BOOK KARNI UKU BOOK 1
AUTHOR MANSUR USMAN SUFI
UPLOADER MRS SUFI NOVELS
IMAGE  SUFI GRAPHICS
SIZE 23KB
FILE TXT
DATE 27 MARCH 2023
GROUP ZAUREN SUFI NOVELS 
TAGES  ADVENTURE

About the Book of Three Centuries contains 
  •  The stories of many Islamic empires, King Khalid ibn Sudeis was a WORLD HERO who developed in Islamic knowledge and bravery, he had a beautiful wife whose beauty spread throughout the world and the Arab continent , 
  • She gave birth to a beautiful young woman who succeeded him, in Islamic knowledge, bravery and talent. 
  •  King Khalid was righteous and compassionate to the poor as well as doing good to the community, he did not accept abuse or oppression, so he became a leader who fights oppression.
STEPS TO DOWNLOAD OUR BOOK. 

  1.  First of all, the person who wants to own our book must confirm that he has an email inbox. 
  2.  Then he seems to have enough data to traffic on the internet.
  3.  You must have a charge on your mobile phone to download the Book safely. 
  4.  We do our best to improve our services for you.

KARNI UKU
BOOK 1 COMPELET
WRITING BY AUTHOR
MANSUR USMAN SUFI
SARKIN MARUBUTAN HAUSA
WTHAPP NUMBER
08137237071

ƘASAR MADINATUL-BARNAWIY

     Kasaitaccen ɗakin taron ya cika ya batse da manyan sarakuna,Bokaye,matsafa haɗe da jarumai.
    Duba ɗaya zaka yi musu ka fahimci cewa akwai wani muhimmin al’amari daya taru a wajen.
    Tsawon daƙiƙa talatin ana cikin wannan hali babu wanda yace ƙala.
     Daga bisani ne wani dattijo ma’abocin ƙasumba da gemu farare sol!, Mai ɗauke da yanayin ɗaure fuska.
   Yayi gyaran murya ya dubi jama’ar dake ɗakin taron yace “yaku yan uwana sarakuna da sauran mahalarta wannan taro mai albarka, dafarko ina yiwa kowa Barka da zuwa.
   Babban abinda ya tara mu anan shine tabbatar da tsafi a doran ƙasa, wanda hakan bazai taɓa tabbata ba face an ɓatar da ma’abota addinin Musulunci a doran ƙasa.
    Sanin kanku ne cewa dakushe hasken musulmi abune mai matukar wahalar gaske, matukar muna son cimma wannan buri namu dole sai mun jefa musulunci cikin saɓon Ubangijinsu.
      Daga lokacin da na fara wannan nazari da sauran Yan uwana sarakuna, mun fara cimma nasarori masu yawa, sai dai a halin yanzu ne zamu kama aikin gadan-gadan ta hanyar haɗa karfi da ƙarfe, domin masu iya magana na cewa hannu ɗaya baya ɗaukar jinka.
     Ubangiji na faɗa a cikin littafinshi mai tsarki cewa “idan Musulmi suka bauta mashi yadda yake so, zai basu rayuwa mai daɗi tare da ‘ya’yansu da jikokinsu.
      Sannan a sunnah ya tabbata cewa su musulmi kamar ginin daƙi ne mai kusurwa huɗu, kowace katanga tana karfafawa ne da yar uwar ta, ma’ana dazarar rabuwar kai ta shiga tsakaninsu kodai ta fahimtar addini ko kabilanci da al'adun yau da kullum,to daga nan zasu samu nasara murƙushe.
     Lokacin da dattijon da ake kira da suna urwat ɗan Abbas yazo Nan azancenshi sai dukkan wanda ke cikin ɗakin taron ya cika matukar mamaki jin yana karanta littafin Allah tamkar yakasance musulmi.
       Urwat ya cigaba dacewa “Dukkaninmu yan uwa ɗaya ne kuma dangi ɗaya, koda akwai babban jinsi da birane,amma kada mu manta abune ɗaya ne ya haifemu shine, tsafi, bautar gumaka.
    Fiye da shekaru arba’ina lokacin ina samartaka, ina rayuwa.
   A cikin musulunci, babu wani abu nasu da bani da sani a kanshi walau ta fuskar ilimin addini ko zamantakewa.

     Lokacin da yazo nan a jawabinshi sai dukkan wanda ke cikin ɗakin taron ya cika da matuƙar farin ciki,urwat ya gyara zama bisa kujerarshi ya, shiru ne ya kuma mamaye ɗakin taron a karo na biyu.
    Sarki sha’aran yayi gyaran murya yace “Bayan dukkan bayanin da sarki urwat ya kawo yanzu, akwai waɗansu muhimman abubuwa da ya kamata mu lura dasu anan, mafi yawan suna burin ganin sabon al’amari na cigaba a wajen su koda ta hanyar karama(almara).
Ko kuwa ta ƙirƙira, bazasu taɓa damuwa ba koda ya saɓa da addinin su zasu ƙarɓeshi hannu biyu, har wasu ma na ganin idan malami baya karama,to bai cika mai tsoron Allah ba.
    Yanzu dukkan shiryen mu sunyi nisa, mun tura dukkannin mutanenmu izuwa biranen manyan dauloli musulmi, bayan sun samu horo akan dukkan da muka ɗora su akai, daga cikin nasarorin da muka samu.
   Akwai kwaɗaitawa mata da son wassanni, koyarwa da mata dubarun zama da mazajen su na tsarin zamani da al’adunmu, Domin gurɓata zaman su da mazajensu.
    Sannan duka Littattafan da muka wallafa Dake yaƙar gaskiyar dake cikin addininsu, yanzu abinda ya rage mana a gaba shine a mako mai zuwa zamu tura rukuni na ƙarshe daga jama’armu ta zasu tafi ƙasashen a matsayin yan gudun hijira, waɗanda a cikin su ne zamu basu muhimman makamai masu barazana ga dukkan wata halitta mai numfashi, gami da sirrikan tsafi.
      Lokacin da sarki sha’aran yazo nan azancenshi sai yayi kowa dake ɗakin taron ya cika da matukar farin ciki maral misaltuwa.
      Daga wannan kowa ya tattare tawagarsa ya fice daga ɗakin taron.

                      *****

    Yanayin gidan sarautar ya ƙawatu ainun da fiye da misaltawa, idan mutum yakai dubanshi izuwa ga wani ɓangare da yafi ko ina ƙawatuwa zai yi arba da kuyangi,barorin,hadimai gami da dakarun shirye cikin shigar yaƙi na ta kai komo,suna aiyuka.
    Wata kuyanga ce matashiya ɗauke da kayan marmari dangin ridda, ayaba da jini, a cikin wani kwandon kaba, ta doshi wata turakar, tana iso masu gadi suka bude mata kofar shiga ta kunna kai izuwa cikin gami da yin sallama.
  Shiru taji batare da an amsa mata ba, kuma tana iya jiyo alamun motsi a turakar,haka dai ta cigaba da tafiya sannu a hankali tana huce kofofin turkar, har ta iso inda take sa rai zataga gimbiya.
   Salati gami da tasbihi ta dunga karantawa a ranta, har idanun ta sun fara cikowa da kwalla, tana mai runtse su tamkar tayi arba da mutuwarta ƙirjinta na bugawa da sauri,ta saki kwandon dake hannun ta kayan marmarin dake ciki suka tarwatse ta hanyar watsuwa a turkar.
    Duk da motsin da ya bayyana na tarwatsewar kayan marmarin, bata sanyasu dawowa cikin hayyacinsu daga saɓon Ubangijinsu ba.
    Da sauri ta juya domin komawa da baya, zuciyar ta cike da matuƙar ɗimauta, taya ya za’a aikata wannan mummunan saɓon Allah a gidan sarautar musulunci, tabbas sai na bayyana wannan al’amari ga mai martaba sarki koda kuwa hakan zai zamo ƙarshen numfashina a duniya.
    Haka dai ta cigaba da tafiya da sauri har tana tuntuɓe, domin ta isa hanyar da zata sadata da fada.
    Fadar ta cika ta batse da manyan fadawa, talakawan gari haɗe dakaru, kowa na zaune cikin ladabi da girmamawa.
     Sarki Anwar na zaune a bisa karagarshi ta mulki,sanye da tufafin alfarma irin na hamshaƙen sarakai, hannunshi riƙe da cazbaha,yana jan addu’o’i,

Ana tafiyar da sha’anin mulki cikin lumana.
    Wani dattijo ma’abocin tarin shekaru da cikar kamala yayi gyaran murya cikin ladabi ya dubi mai martaba sarki yace”ya shugabana ina wani labari da na samu daga shugaban masu kula da hidimar masallaci cewa, kwana biyu an samu raguwar matasan mu wajen fitowa sallar asubahi, Haƙiƙa hakan babban abin takaici ne sosai,a shawarata kodai a faɗakar da iyaye illar Hakan ko kuwa a sanyawa dukkan wanda yaƙi fitowa sallar asubahi haraji matsawar bada wani uzuri da addini ya amince dashi ba.
      Wani mutum daga cikin fadawan sarki da shekarunshi basu gaza arba’in ba, yayi gyaran murya yakawo Gwauron numfashi ya ajiye ya dubi dattijo mai suna Salman yace” Allah ya shugaban majalissa a rawa fahimtar a cikin littafi da sunna, babu wani waje da ake iya tilasta mutum ibada, ballantana ace idan yaƙi yi a sanya mashi haraji, domin ita ibada ana yin ta ne cikin daɗin rai .
      Ko da jin wannan batu daga bakin Hakimi urwat sau fadar tayi shiru tamkar mutuwa ta kawo ziyara, duk wannan tattaunawa da ake yi sarki yana ji bai ce uffan ba, sai da ya fahimci tattaunawar zata haifar da damuwa, sai yayi gyaran murya yace” yaku fadawana kuyi sani cewa wannan magana da shugaban majalisa ya kawo na da matukar muhimmanci ainun sai dai ni akwai wata matsala dake ganin tana gaba da wannan kuma dare da rana da ita nake tashi,wannna matsala ba wata ba face yawaitar yan gudun hijira daga waɗansu birane dake zuwa wannan ƙasa tamu, domin samun mafaka, hakan baya rasa nasaba da tashe-tashen hankula da ake samu a birnin Nuraniyyu.
      A makon da ya gabata labari ya riskeni cewa a wannan makon an kai wani mummunan hari a masallaci a lokacin da ake gudanar da sallar asubahi, tabbas wannan abun baƙin ciki ne da damuwa daya kamata mu kula sosai ta hanyar ƙarfafa tsaro tare da ba wa mayakan mu horon yaƙi.
  Uwa uba kuma shine tsayawa bisa tafarkin da magabata suka ɗora mu akai…..!
     Kafin sarki ya ƙarshe maganar sai ya hango kuyanga ihsan ta shigo fadar hankalin ta a tashe tana haki,tamkar numfashinta zai ƙare.
      Sarki Anwar ya mayar da dubanshi izuwa gareta domin yaji shin mene ne ke tafe da ita.
      Lokacin da yazamana cewa saura taku huɗu tsakanin ta da karagar mulki sai ta zube ƙasa bisa gwiwoyinta ta kwashi gaisuwa.
      Sarki ya ƙarɓi gaisuwar cikin annuri.
      Ihsan ta buɗi baki ta buɗi baki da nufin tace wani abu amma koda ta haɗa idanu da Hakimi urwat sai taji bakinta yakasa furta komai, tsawon daƙiƙa ashirin tana ƙoƙarin hakan amma ya gagara, Al'amarin da ya sanya sarki da sauran jama'a suka cika da mamaki kenan bisa ganin tana magana da Yaren kurame.
     Sarki ya dubeta yace" yake ihsan shin ina dalilin wannan hali da kike ciki, me kike son fahimtar dani?.
    Hawaye ne ya shiga shata ta daga idanun ta bisa ganin halin da take ciki, tana mai tambayar kanta akan ranta tana mai mai cewa shin ina dalilin rashin yin maganata, koda wani ne yayi mini wani sihiri, amsar tambayar da ta kasa bawa kanta kenan.
    Urwat ya saci kallonta gami da murmushin mugunta, wanda waziri ne kaɗai ya lura da hakan.
     "Ta yiwu akwai wata rashin lafiya ce ta same ta, ranka ya daɗe ina ganin yana da kyau mu tafi zuwa masallaci domin lokacin sallar azuhur yayi.
    Hakimi urwat ya faɗa cikin ladabi".
    " Zancen ka dutse yakai urwat".
    Sarki ya faɗa tare da kallon in da hasken rana ya ratso a fadar.
       Ya ɗorawa batun shi da cewa "A kai ihsan izuwa wajen 'yar mai ganye domin a duba lafiyarta, Ka dawo da ita izuwa gareni, haƙiƙa na tabbata akwai wani muhimmin al'amari da take son sanar dani, domin na aminta da ita matuƙa.
      Ya ƙare zancenshi yana duban wani bafade, saurayin mai yanayin kazar-kazar dake tsaye a hannunshi na dama.
     " An gama ya shugabana Bafaden ya daɗi cikin ladabi, ya juya ya nufi kofar fita daga fadar taɓa mai yafito ihsan da hannu dake yi mata nuni ta biyo bayanshi, Da sauri ta miƙe tsaye tayi koyi dashi suka kule izuwa wajen fadar.


ALSO RELATED POST


{getButton} $icon={download} $text={DOWNLOAD NOW}

Post a Comment

Previous Post Next Post